Lai Mohammed, ya yi kira da a soke rijistar ’ya’yan jam’iyyar APC da ake gudanarwa a Jihar Kwara.

Ministan Watsa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed, ya yi kira da a soke rijistar ’ya’yan jam’iyyar APC da ake gudanarwa a halin yanzu a Jihar Kwara.

Ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ’yan jarida ranar litinin a mahaifarsa dake Oro, inda ya yi zargin cewa jami’an da aka tura don yin rijistar jam’iyyar a jihar sun karya ka’idojin da uwar jam’iyar ta kasa ta shimfida.

Ministan ya kuma ce kwamatin ya karya sharudan da aka gindaya na rarraba kayan gudanar da aikin rijistar ’ya’yan jam’iyyar a fadin jihar.

Ministan ya bukaci a soke baki dayan rijistar a fadin Jihar ta Kwara har sai an tabbatar da yin rijistar kamar yadda jam’iyyar ta tsara kuma yadda kowa zai gamsu da tsarinta.

Check Also

IMG Spraker Falgore

Capacity building ; a morale booster for effective service delivery.. Speaker Falgore.

From the Legislative House, Kano State House of Assembly. Capacity building ; a morale booster …