Gwamnatin Tarayya ta gargadi ’yan kasar akan sake bullar cutar Ebola a makwabtan kasashe

Gwamnatin Tarayya ta gargadi ’yan kasar nan cewa bullar cutar Ebola a makwabtakan kasar na barazana gare ta, yayin da aka gano masu dauke da sabon nau’in cutar COVID-19 mai saurin kisa a kasar.

Shugaban Kwamitin yaki da COVID-19 (PTF) kuma Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha ya ce kasar nan za ta tsaurara matakan tantance lafiya a hanyoyin shiga kasarta musamman daga kasashen Guinea da Congo da aka samu bullar cutar Ebola.

Boss Mustapha ya kara da cewar wannan nauyi ne ba a kan gwamnati kadai ba, daukacin ’yan kasar nan da sauran jama’a ma na da rawar da za su taka.

Check Also

IMG Spraker Falgore

KNHA okays Governor Abba Kabir to appoints 25 Special Advisers

KNHA okays Governor Abba Kabir to appoints 25 Special Advisers The State House of Assembly …