Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum bakwai a yankunan jihar sakamakon hare-haren ‘yan fashi. Kwamishinan Tsaron jihar Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan a jiya Lahadi, inda ya ce ‘yan bindigar sun hallaka mutum biyu a ƙauyen Kajinjiri na Ƙaramar Hukumar Igabi sannan an raunata mutum ɗaya kuma …
Read More »Gwamnan Kano ya sanar da bayar da tallafin Naira miliyan uku ga mutumin da ya rasa iyalai bakwai a sakamon gobara domin rage radadinta.
Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da bayar da tallafin Naira miliyan uku ga Malam Abdulrahman Ibrahim Wailari, mutumin da ya rasa iyalai bakwai a sakamon gobara domin rage radadinta. Mutumin dai mazaunin unguwar Wailari a Karamar Hukumar Kumbotso ya rasa iyalan nasa ne sakamakon wata gobara …
Read More »Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci wadanda suka tsinci kansu cikin iftila’i daba-daban a jihar Kano dasu hanzarta yin rijista…
Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci wadanda suka tsinci kansu cikin iftila’i daba-daban a jihar Kano dasu hanzarta yin rijista da hukumar tallafawa gajiyayayu ta jihar Kano domin cin gajiyar tallafin gwamnatin tarayya. Gwamna Ganduje ya bayyana hakane a yammacin jiya yayin rabon kayayyakin tallafi ga yan asalin …
Read More »AUFCDN: Yajin aikin da dillalan kayan abinci suka fara na ƙungiyar ya janyo tashin farashin kayayyaki a yankin kudancin kasarnan.
Rahotanni sun bayyana cewa, yajin aikin da dillalan kayan abinci suka fara na ƙungiyar Amalgamated Union of Foodstuff and Cattle Dealers of Nigeria AUFCDN, ya janyo tashin farashin kayayyaki a yankin kudancin kasarnan. Ƙungiyar ta AUFCDN wadda ɓangare ne na ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa wato NLC, ta fara yajin aikin …
Read More »Kamfanin man fetur na kasa NNPC ya musanta zargin da ake cewa yana shirin ƙara farashin litar mai a ƙasar.
Kamfanin man fetur na kasa NNPC ya musanta zargin da ake cewa yana shirin ƙara farashin litar mai a ƙasar. Shugaban kamfanin Malam Mele Kyari a hirarsa da BBC ta wayar tarho, ya bayyana cewa ƴan kasuwa ne suka jawo dogayen layuka a gidajen mai a wasu sassan ƙasarnan bisa …
Read More »Jami’ar Oxford ta ce an yi kutse a ɗaya daga cikin ɗakunan gwajin da take bincike kan cutar korona.
Jami’ar Oxford ta ce an yi kutse a ɗaya daga cikin ɗakunan gwajin da take bincike kan cutar korona. Wani mai bincike kan harkokin tsaro a Birtaniya, Alex Holden, ya ce masu kutsen sun riƙa magana da Harshen Portuguese, kuma da alama sun aikata hakan ne daga Kudancin Amurka. Wani …
Read More »Shugabancin kasuwar farm center dake yankin karamar hukumar Tarauni yasha alwashin hada kai da karamar hukumar Tarauni…
Shugabancin kasuwar farm center dake yankin karamar hukumar Tarauni yasha alwashin hada kai da karamar hukumar Tarauni dan kawo cigaba mai ma’ana a fadin karamar hukumar da kasuwar baki daya Da yake jawabi yayin wata ziyara da suka kaiwa sabon shugaban karamar hukumar Abubakar Zakari Muhammad a ofisinsa a madadin …
Read More »Ma’aikatar muhalli ta jihar kano ta jinjinawa hukumar kare faruwar hadura ta kasa reshan jihar kano
Ma’aikatar muhalli ta nan jihar kano ta jinjinawa hukumar kare faruwar hadura ta kasa reshan jihar kano, bisa yadda suka himmatu wajan tsaftace muhallin su a koda yaushe. Kwamishinan ma’aikatar muhalli ta nan kano Dr. Kabiru Ibrahim Getso shine ya bayyana hakan a lokacin rangadin aikin tsaftar muhalli mai kula …
Read More »Sokoto: Daruruwan iyalai ne suka arce daga kauyukansu saboda yadda ‘yan fashi,,,
Rahotanni daga gabashin jihar Sakkwato na cewa daruruwan iyalai ne suka arce daga kauyukansu saboda yadda ‘yan fashin da suka dauki kwanaki suna kai musu hare-hare babu ƙaƙƙautawa. Wasu da lamarin ya shafa sun shaida wa manema labarai cewa akwai dubban mutane da a yanzu haka ke fakewa a wata …
Read More »UNICEF: ta bayyana sace ɗaliban makarantar sakandare ta GGSS Jangebe a Jihar Zamfara da cewa “abin ɓacin rai ne”.
Asusun Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya bayyana sace ɗaliban makarantar sakandare ta GGSS Jangebe a Jihar Zamfara da cewa “abin ɓacin rai ne”. Cikin wata sanarwa da Wakilin asusun UNICEF a kasar nan Peter Hawkins ya fitar ya ce kamata yayi a ce yara na cikin aminci a …
Read More »